Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Mutane 4 sun mutu a ruftawar gini a Najeriya
2019-10-14 10:15:10        cri
Hukumar bada agajin gaggawa a Najeriya ta ce mutane 4 ne suka mutu wasu 6 kuma suka jikkata a sanadiyyar ruftawar gini a jahar Legas cibiyar kasuwancin kasar.

Femi Oke-Osanyintolu, janar manajan hukumar bada agajin gaggawa ta jahar Legas ya shedawa kafafen yada labarai cewa, al'amarin ya faru ne a ranar Asabar din da ta gabata a sakamakon mamakon ruwan sama da aka sheka a yankin.

Ya ce wata mace da 'yayanta uku sun mutu a sanadiyyar ruftawar ginin sai dai mijin matar ya tsira da ransa.

Oke-Osanyintolu ya ce, ginin dake kan tudu ne ya rufto kan wani gida dake kasa, sai dai a cewarsa ba'a tabbatar da adadin mutanen da birabizan ginin ya danne ba, amma masu aikin ceto suna cigaba da gudanar da ayyukansu.

Wani kwararre a yankin ya ce, ana yawan samun matsalolin ruftawar gini a Najeriya sakamakon yadda wasu masu tsara gine gine basa mutunta dokokin da suka shafi aikin tsara gine ginen.

A mafi yawan lokuta, ana jibga abubuwa masu nauyin gaske a saman ginin, kuma a wasu lokutan ana amfani da kayayyakin gini marasa inganci. (Ahmad)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China