Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Manzon musamman na shugaba Xi Jinping ya halarci taron makokin Mugabe
2019-09-15 16:40:53        cri
Manzon musamman na shugaban kasar Sin Xi Jinping kuma mataimakin shugaban majalisar bada shawara kan harkokin siyasa ta kasar Sin Gu Shengzu ya halarci taron zaman makokin tsohon shugaban kasar Zimbabwe Robert Mugabe jiya a birnin Harare. A madadin shugaba Xi Jinping, da gwamnatin kasar Sin da kuma jama'arta, Gu Shengzu ya bayyana juyayin mutuwar marigayi Mugabe, yana mai jajantawa shugaban kasar Zimbabwe na yanzu Emmerson Mnangagwa, da jama'ar kasar, da kuma iyalan marigayi Mugabe.

A yayin ziyararsa a kasar Zimbabwe, Mr Gu ya gana da shugaban kasar Mnangagwa, inda ya bayyana cewa, marigayi Mugabe dan siyasa ne da ya jagoranci 'yantar da al'ummar kasar, da samar da gudummawa sosai wajen sa kaimi ga hadin gwiwar dake tsakanin kasarsa da kasar Sin, da kuma tsakanin Afirka da Sin baki daya. Ya ce, kasar Sin ba za ta manta da wannan aboki ba. Kana Sin na son hada hannu da kasar Zimbabwe wajen sa kaimi ga raya dangantakar abota ta hadin gwiwa dake tsakaninsu a dukkan fannoni.

A nasa bangare, shugaba Mnangagwa ya bayyana cewa, tara manzon musamman da shugaba Xi Jinping ya yi don halartar taron makokin Mugabe, ya shaida cewa, akwai sada zumunci mai karfi tsakanin jama'ar kasashen biyu, kuma kasarsa za ta ci gaba da zurfafa hadin gwiwar dake tsakaninsu a nan gaba. (Zainab)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China