2019-08-27 09:49:58 cri |
Masu zanga-zangar, dauke da tutocin kasar Sin da Kyallaye suna kiraye kiraye, sun fara zanga-zangar ne da rana, daga Chater Garden dake yankin tsakiyar HK zuwa ofishin jakadancin Amurka.
Tsao Tat-ming, wanda ya shirya zanga-zangar, ya ce suna kokarin gina HK, yayin da bata-gari ke lalata ta, kuma akwai masu ingiza su. Yana mai nuna Amurka a matsayin wadda ke da hannu wajen ta'azzarar rikicin baya-bayan nan a yankin.
A cewarsa, zanga–zangar wadda mutane daga kungiyoyi daban-daban suka shiga, na da nufin yin tir da yadda Amurka ta tsoma baki cikin harkokin cikin gidan kasar Sin.
Masu zanga-zangar sun kuma bayyana goyon bayansu ga kokarin 'yan sandan HK na tabbatar da zaman lafiya yayin da ake tsaka da gudanar da zanga-zangar. (Fa'iza Mustapha)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China