Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Gwamnatin yankin Hong Kong ta ce zanga-zangar da ake yi ta wuce iyaka, kuma ba za a lamunci keta dokoki ba
2019-08-05 10:19:53        cri

Kakakin gwamnatin yankin musammam na Hong Kong na kasar Sin, ya bayyana a jiya cewa, zanga –zangar da ake yi a yankin a baya-bayan nan, ya zarce iyakar lumana, don haka gwamnatin da daukacin al'umma ba za su amince da ita ba.

Da yake tsokaci kan tabarbarewa zanga-zangar, kakakin ya bayyana cikin wata sanarwa cewa, keta dokoki da hana al'umma kwanciyar hankali da kai hare-hare kan 'yan sanda za su illata yankin da tattalin arzikinsa da kuma zaman rayuwar jama'a.

Ya ce zanga-zangar da aka shirya domin bayyana bukatu, ta sa an kara kaimi kan toshe tituna da sauran wasu abubuwan da suka sabawa doka. (Fa'iza Mustapha)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China