Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Kasar Sin za ta zuba jarin Yuan miliyan 2 kan kowanne filin kwallo
2019-07-31 14:12:20        cri
A cewar wani daftari da hukumar raya kasa da gyare gyare ta kasar Sin ta fitar a hukumance da hadin gwiwar hukumar kula da wasanni da kungiyar kwallon kafa ta kasar Sin, ya ce Gwamnatin tsakiyar kasar Sin za ta samar da tallafi ga aikin gina sabbin filayen Ball a kasar.

A cewar daftarin, za a samar da tallafin kudi ga aikin gina sabbin filayen kwallo da fadinsu ke daukar 'yan wasa 11-11 a kowanne bangare da Yuan miliyan 2 kowanne, kwatankwacin dala 290,600. Sannan game da sabbin filaye masu daukar 'yan wasa 5-5 da masu daukar 7-7 a kowannen bangare, gwamnatin kasar za ta ba da kudin Yuan miliyan 1 bisa kowannensu. An gabatar da matakin ne domin masu kaunar kwallon kafa su samu saukin samun ingantattun filayen kwallo, tare da rage kudaden da suke kashewa. (Fa'iza Mustapha)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China