Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Gwamnatin tsakiya na sanya ido game da yanayin da ake ciki a yankin Hong Kong na Sin, in ji Yang Guang
2019-07-29 19:42:27        cri
Kakakin ofishin dake lura da al'amuran da suka shafi yankunan Hong Kong da Macao, karkashin majalissar zartaswar kasar Sin Yang Guang, ya ce gwamnatin tsakiyar kasar Sin, na matukar sanya ido game da halin da ake ciki a yankin na Hong Kong.

Yang Guang, ya bayyana hakan ne a Litinin din nan, biyowa bayan zanga zanga da yamutsi, da suka auku a yankin musamman na Hong Kong, yayin da yake tsokaci gaban taron 'yan jaridu da ya gudana a nan birnin Beijing.

Jami'in ya ce, 'yan sandan Hong Kong sun amince, tare da ba da kariya ga masu zanga zanga cikin lumana bisa doka, sakamakon rashin amincewar da ta biyo bayan dokar mika masu manyan laifuka babban yankin Sin domin fuskantar hukunci, da ma batutuwa masu nasaba da samun tallafin shari'ar da ta shafi hakan.

To sai dai kuma, Yang ya ce karya dokoki da wasu tsageru suka rika yi tun daga ranar 12 ga watan Yuni, ya zarta batun zanga zanga. Ya ce tarzoma da yamutsin a yankin Hong Kong sun haura wata daya, lamarin da ya haifar da karya doka da oda, da gurgunta yanayin zamantakewa, da tattalin arziki, da ma kwanciyar hankalin al'ummar yankin. (Saminu)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China