Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Kasar Sin ta bayyana kudurinta na taimakawa yankin Xinjiang
2019-07-17 11:14:46        cri

Mamban zaunannen kwamitin hukumar siyasa na kwamitin koli na Jam'iyyar Kwaminis ta kasar Sin, kana jami'in tsare-tsare na kwamitin koli JKS game da aikin raya yankin Xinjiang Wang Yang, ya jaddada shirin kasarsa na baiwa yankin Xinjiang tallafi na dogon lokaci, ta hanyar wani shirin ba da tallafi, wanda za a aiwatar da manufar jam'iyya game da tafiyar da harkokin yankin na Xinjiang a sabon zamani

Jami'in ya bayyana hakan ne yayin taron tallafawa yankin karo na 7 da ya gudana a Hotan, dake kudancin yankin Xinjiang na Uygur mai cin gashin kansa.

Wang ya ce, shirin zai taimaka wajen bullo da wata sabuwar hanyar raya yankin, da ba da gudummawa ga ci gaban tattalin arziki da inganta rayuwar jama'a, zai kuma taimaka wajen hada kan mazauna yankin baki daya.

Tun a shekarar 1997 ne dai kasar Sin ta fara aiwatar da shirin taimakawa yankin Xinjiang, inda sauran yankunan kasar ke tattara kudade don taimakawa yankin da tura ma'aikata da kwararru don su yi aiki su kuma rike mukamai na wasu lokuta a wurin.(Ibrahim)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China