![]() |
|
2019-07-12 10:53:04 cri |
Coumba Gadio, ta ce auren wuri ga yara kanana na kunshe da keta hakkokin yara, yana kuma ba da damar keta hurumin 'yan mata masu kananan shekaru, baya ga hadarin kamuwa da cututtukan jima'i, ciki hadda HIV ko Sida tsakanin yara masu karancin shekaru.
Jami'ar ta bayyana hakan ne, yayin taron kwamitin tawagogin kasashe da na kungiyoyi daga kwamitin gudanarwar asusun MDD mai kula da yawan al'umma ko UNFPA a takaice, da takwarorin su na asusun kananan yara na MDD UNICEF, da shirin kasa da kasa game da gaggauta matakan kawo karshen auren wuri ga yara.
Kwamitin dai ya yi tarukan sa na masu ruwa da tsaki a wannan karo a kasar Zambia ne, da nufin zakulo hanyoyin dakile kalubalen aurar da yara masu karancin shekaru a sassan duniya. (Saminu Alhassan)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China