![]() |
|
2019-05-31 10:48:02 cri |
An ba da labari cewa, a gun taron koli na 'yan mata da aka yi a shekarar 2015, shugaba Xi ya sanar da gayyatar 'yan mata dubu 30 daga kasashe masu tasowa don su kara ilmi a kasar Sin. Aikin ba da ilmi na digiri na biyu da kwalejin ya gabatar mai taken "Dangantaka tsakanin karfin jagoranci na mata da bunkasuwar al'umma ", ya kasance matakin da ya tabbatar da wannan buri na shugaba Xi.
A kwanakin baya, wasu dalibai sun mika wata wasika ga shugaba Xi da Madam Peng don bayyana ci gaban da suka samu wajen karatu, da mika godiya gare su da taimakon da Sin ke ba su.
A cikin ganawar da aka yi a wannan rana, Madam Peng ta furta cewa, Sin na dora muhimmanci sosai kan ayyukan mata, kuma tana fatan kara hadin kanta da kasashen duniya don ingiza wannan aiki yadda ya kamata. (Amina Xu)
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China