Bayan gaisuwa mai yawa da fatan alheri ga ma'aikatan ku baki daya a birnin Beijing. Bayan haka, ina mai gabatar da sakon jaje na ga al'ummar Sinawa musamman wanda ke lardin Yunnan dake kudu maso yammacin kasar Sin bisa annobar girgizar kasa da ta aukawa garin. Lamarin da kawo asarar rayuka kimanin 589 a yayin da fiye da 1000 suka jirkata.
Ina jajantawa wadanda suka yi asarar 'yan uwansu da wadanda suka tsira da raunuka har ma da wadanda suka yi asarar dukiyoyinsu. Da fatan ba za a sake samun aukuwar wannan bala'i ba, nake yi musu fatan alherin saurin farfadowa daga wannan tashin hankali tare da maye gurbin dimbin asarar da suka tafka sakamakon wannan girgizar kasa.
Mai sauraronku a kullum
Nuraddeen Ibrahim Adam
Kanon Dabo, Nigeria