Bisa kokarinsa, da na shugaban asibitin sada zumunci tsakanin Sin da Guinea, Fodé Ibrahima Camara, an kammala wannan horaswa lami lafiya. Likita Camara ya nuna babban yabo ga rukunin likitocin Sin a Guinea karo na 24 a karkashin jagorancin malam Wang, ya ce, "Mun gamsu sosai da gudummawar da gwamnatin Sin da rukunin likitocinta suka bayar gare mu. A lokacin da ake kokarin shawo kan cutar Ebola, gwamnati da jama'ar kasar Sin suna kasancewa tare da jama'ar Guinea a ko da yaushe. Ban san hakikanin jimillar kudin da gwamnatin Sin ta kashe domin taimakawa ba, amma na san cewa, ta ba da agaji a duk fannoni, kamarsu kudi, da kayayyaki, da ma'aikata da sauransu. Zuwan rukunin likitocin Sin ya taimaka sosai wajen ingnata kiwon lafiyar mu." (Fatima)