in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Zanga-zangar ranar 4 ga watan Mayu ta karfafa farfadowar kasar Sin
2019-04-30 11:07:51 cri

Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya ce karfin zanga-zangar ranar 4 ga watan Mayu, ya karfafa buri da yakinin al'ummar Sinawa da ma kasar, na samun farfadowa.

Shugaban Xi Jinping, ya bayyana haka ne a yau Talata, yayin taron da aka yi don cikar zanga-zangar shekaru 100 da gudana.

Ya ce zanga-zangar muhimmin gangami ne na kishin kasa da juyin juya hali da matasa 'yan boko suka assasa, inda kuma al'ummar kasar daga ko wane bangare na rayuwa suka shiga aka dama da su wajen yaki da mulkin kama karya.

Xi Jinping ya ce ta kuma wayar da kai game da sabbin hanyoyin yada akidu da al'adu da kuma ilimi. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China