in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Xi Jinping: Ya kamata a kara nazari kan zanga-zangar Ranar 4 ga Watan Mayu na Shekarar 1919
2019-04-20 17:03:54 cri
Ofishin siyasa na kwamitin tsakiya na jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin ya gudanar da taro a jiya Juma'a, don tattaunawa kan ma'anar tarihi ta zanga-zangar Ranar 4 Ga Watan Mayun Shekarar 1919, da kuma darajarta.

A yayin tattaunawar, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya jaddada cewa, batun muhimmiyar alama ce a tarihin zamanin da da na yanzu. A cewarsa, a yayin da ake tunawa da ranar, dole ne a kara nazarinta da jagorantar matasan kasar Sin da su yi kokari bisa tunanin abun da ya faru, don kafa zaman al'umma mai matsakaicin karfi, da raya tsarin gurguzu da ke da halin musamman na kasar Sin, da kuma cimma burin farfado da al'ummar kasar Sin.

A ranar 4 ga watan Mayun shekarar 1919 a nan birnin Beijing, aka tayar da wata zanga-zangar kishin kasa, wadda ke adawa da mulkin mallaka da wasu manyan kasashen duniya masu fada a ji suka gudana a nan kasar Sin, da tsarin mulkin kama karya, inda dalibai matasa na jami'o'i tare kuma da wasu fararen hula, da mazauna birnin da 'yan kasuwa da masu tafiyar da masana'antu suka halarta tare. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China