in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sudan ta kudu za ta fara hako gangar danyen mai 70,000 a kullum daga watan Yuni
2019-04-01 10:21:59 cri

Ma'aikatar kula da albarkatun mai ta kasar Sudan ta kudu ta sanar cewa nan da watanni masu zuwa za ta dawo da aikin hako mai a rijiyoyin man kasar uku da aka dena aikin inda ake fatar hako gangar danyen mai dubu 70 a kullum nan da watan Yuni.

Ma'aikatar man fetur da hakar ma'adinai ta kasar ta fada cikin sanarwar cewa, yankunan masu albarkatun mai na El-Nar, El-toor da Manga, dukkan yankunan suna arewacin kasar ne za su fara aikin hako man daga ranar 27 ga watan Afrilu, tare ta alwashi hako gangar danyen mai 70,000 a kullum zuwa watan Yuni.

Wannan matakin ya biyo bayan wani rangadi ne da ministan albarkatun mai na Sudan Ezekiel Lol Gatkuoth da takwaransa na kasar Sudan Ishag Adam Bashir Gamaa suka kai zuwa yanki mai arzikin mai na kasar a ranar Asabar.

Gatkuoth ya bukaci kamfanin hakar mai na kasar, wanda ke gudanar da aikin gyaran rijiyoyin mai na El-Nar da El-toor, da ya gaggauta kammala aikin domin cimma wa'adin da aka diba na dawo da aikin hakar man a ranar 27 ga watan Afrilu.

Ministocin biyu sun sanya hannu kan yarjejeniyar amincewa don baiwa kamfanonin dake aikin hakar man a Sudan ta kudu da su yi amfani da yankunan kasar Sudan wajen yin jigilar kayayyakin aikin hako albarkatun man. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China