A jawabin da ya gabatar yau, a yayin taron dandalin tattaunawar Asiya ta Boao a lardin Hainan, Li Keqiang, firaministan kasar Sin ya ce, tabbas kasar Sin za ta cika alkawarin da ta yi na rage yawan haraji da wasu kudade da ake biya. Wannan kyakkyawan mataki ne da kasar Sin take dauka kai tsaye ta fuskar yin gyare-gyare a gida, a kokarin tabbatar da adalci da kuma kawo wa dukkan al'umma alheri. Haka kuma muhimmin mataki ne da kasar Sin take dauka a bana, a kokarin sakarwa kasuwa mara yadda ya kamata, da hana koma bayan tattalin arziki. (Tasallah Yuan)