Kasar Sudan ta kudu ta daddale wata yarjejeniya da kamfanin kasar Sin wato rukunin Shandong Hi-Speed domin gudanar da aikin gina wasu manyan hanyoyin mota a kasar wadanda za su hade yankunan karkara na kasar da babban birnin kasar Juba.
Rebecca Joshua Okwaci, ministar kula da hanyoyin mota da gadoji ta kasar ta bayyana cewa, aikin zai taimaka wajen kyautata zaman lafiya, baya ga taimaka wajen bunkasa ciniki, aikin zai kuma taimaka wajen sada zumuntar al'ummar kasar bayan shafe shekaru biyar ana fama da tashin hankali a kasar.(Ahmad Fagam)