in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin da Masar za su karfafa hadin gwiwarsu a fanni tsaro
2019-03-26 10:01:01 cri

Shugaban kasar Masar, Abdel Fattah al-Sisi, ya lashi takobin kara karfafa hadin gwiwar tsaro da kasar Sin, yayin da yake ganawa da mamban majalisar gudanarwar kasar Sin kuma ministan tsaron kasar, Wei Fenghe dake ziyara a Masar.

Yayin ganawar a jiya Litinin, Abdel Fattah al-Sisi, ya tunatar da dadewar dangantakar dake tsakanin Sin da Masar, inda kasashen biyu suka samu kyawawan sakamako a dukkan fannoni, yana mai bayyana irin gudunmuwar da Sin ke bayarwa ga zaman lafiya a duniya.

Ya kuma jinjinawa nasarorin da kasar Sin ta samu a ci gabanta, yana mai cewa, Masar na goyon bayan shawarar Ziri Daya da Hanya Daya, kuma yana sa ran kara karfafa hadin gwiwa da kasar Sin a fannin ginin ababen more rayuwa.

Shugaba al-Sisi ya kuma bayyana fatan bangarorin biyu za su inganta hadin gwiwarsu a bangaren tsaro da kara hadin gwiwa a fannonin yaki da ta'addanci da horon kwancen soji domin karfafa aikin soji da ma bangaren tsaro.

A nasa bangaren, Wei Fenghe, ya ce kasar Sin na yabawa muhimmiyar rawar da Masar ke takawa a batutuwan da suka shafi shiyyarta da kuma kasa da kasa, kana tana goyon bayan kokarin Masar na kare cikakken iko da 'yancinta.

Jami'in na kasar Sin ya kara da cewa, a shirye kasar Sin take ta kara hada hannu da Masar domin inganta shawarar Ziri Daya da Hanya Daya da nufin kara habaka dangantakar dake tsakaninsu. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China