in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ministan harkokin wajen Tanzaniya ya yi kira a bunkasa alakar tattalin arziki
2019-03-25 08:55:27 cri
Sabon ministan harkokin waje da hadin gwiwar kasashen gabashin Afirka na kasar Tanzaniya Palamgamba Kabudi, ya bukaci jakadun kasar dake kasashen ketare da su bunkasa tattalin arzikin kasar.

Kabudi wanda ya bayyana hakan yayin da ya ke jawabi ga kungiyar ma'aikata dake aiki a ma'aikatarsa a Dodoma, babbar birnin kasar, ya ce ya kamata jakadun kasar dake ketare su ba da muhimmanci wajen kulla alakar tattalin arziki da sauran kasashe. Daga nan sai ya bukaci ma'aikata dake aiki a ma'aikatarsa da su gudanar da ayyukansu bisa hakki da gaskiya, ta yadda za su yi goyayya a diflomasiyar kasa da kasa.

Ya ce, ya kamata jakadun kasar dake ketare su taimaka wajen zakulo masu sha'awar zuba jari, da masu yawon shakatawa zuwa kasar da nemo kasuwannin da za a rika sayar da amfanin gonan da ake nomawa a kasar.

A ranar 3 ga watan Maris din wannan shekara ce dai, shugaba John Magufuli na kasar Tanzaniya ya maye gurbin Augustine Mahiga da Kadubi a matsayin ministan harkokin waje. Yayin Mahiga ya zama sabon ministan harkokin shari'a da kundin tsarin mulkin kasa.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China