in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ba ta ji dadin yadda Amurka take tsoma baki cikin harkokin Hong Kong
2019-03-22 19:51:55 cri

Yau Jumma'a 22 ga wata, Geng Shuang, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin ya bayyana rashin jin dadin kasarsa da kuma kin yarda da sukar da ma'aikatar harkokin wajen kasar Amurka ta yi wa gwamnatin kasar Sin da ma hukumar yankin musamman na Hong Kong cikin rahotonta na shekara-shekara kan manufofin Hong Kong.

Geng Shuang ya nuna cewa, tun bayan da aka maido da Hong Kong karkashin shugabancin kasar Sin, ana aiwatar da manufar "kasa daya, tsarin mulkin biyu" a Hong Kong, inda kuma mazauna yankin Hong Kong suke tafiyar da harkokinsu da kansu, kana ana kare hakkinsu da kuma 'yancinsu. Manufar gwamnatin Sin ta tafiyar da harkoki bisa kundin tsarin mulkin kasa da manyan dokokin Hong Kong da kuma bin manufar "kasa daya, tsarin mulki biyu" ba za ta sauya ba. (Tasallah Yuan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China