in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Amurka ta nuna goyon bayan warware batun Syria ta hanyar siyasa karkashin jagorancin MDD
2019-03-07 11:04:00 cri
Ma'aikatar harkokin wajen kasar Amurka ta bayyana a jiya Laraba 6 ga wata cewa, sakataren ma'aikatar Mike Pompeo ya bayyana cewa, kasar Amurka ta nuna goyon bayan warware rikicin Syria ta hanyar siyasa karkashin jagorancin MDD.

Pompeo ya gana da manzon musamman mai kula da batun Syria na babban sakataren MDD Geir Pedersen a ranar 5 ga wata a birnin Washington, inda suka tattauna shirin warware batun Syriar. Pompeo ya bayyana cewa, gwamnatin kasar Amurka ta nuna goyon baya ga MDD da ta yi kokarin warware rikicin Syria ta hanyar matakan siyasa, wadanda suka hada da ayyukan yin kwaskwarima kan kundin tsarin mulkin kasar Syria, da yin shirye-shirye don gudanar da zaben shugaban kasar cikin 'yanci da adalci da sauransu. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China