in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Tsohon firaiministan Sao Tome da Principe zai jagoranci tawagar AU a zaben Guinea-Bissau
2019-03-05 09:55:01 cri

Kungiyar tarayyar Afrika (AU) ta sanar a jiya Litinin cewa, tsohon firaiministan kasar Sao Tome da Principe, Joaquim Rafael Branco, zai jagoranci tawagar AU mai sa ido a zaben da za'a gudanar a jamhuriyar Guinea-Bissau a wannan mako.

Ana sa ran tagawar ta AU za ta sanya ido kan zaben majalisar dokokin Guinea-Bissau, wanda aka shirya gudanarwa a ranar 10 ga watan Maris.

Tawagar sa idon ta AUEOM, wadda Branco ke jagoranta, ta kunshi jami'an sa ido kimanin 30 wadanda aka tura don sanya ido a zaben majalisar dokokin kasar ta Guinea-Bissau wanda aka fara shirye shiryensa tun a ranar 2 zuwa 16 ga watan Maris, wata sanarwa daga AU ne ta tabbatar da hakan a jiya Litinin.

A cewar kungiyar ta AU, babbar manufar shirin sa idon a zaben ita ce don ba da gudunmowa wajen kyautata zaman lafiya da kwanciyar hankali a Guinea-Bissau da ma Afrika baki daya.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China