in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Guinea-Bissau ya sanar da rushe gwamnati
2016-11-15 11:19:08 cri

Shugaban kasar Guinea-Bissau Jose Mario Vaz ya sanar a ranar Litinin, a cikin wani jawabi zuwa ga 'yan kasarsa, da rushe gwamnatin firaminista Baciro Dja, da nada wani sabon firaministan da zai samu amincewar kowa cikin sauri.

Wannan sabon faraminista, a cewar shugaban kasar, za a daura masa nauyin kafa wata gwamnatin hadaka, kamar yadda yarjejeniyar Conakry ta tanada, domin fitar da Guinea-Bissau daga ricikin siyasa da zaman zullumi na fiye da shekara guda.

A cikin jawabin nasa, shugaba Vaz ya bayyana cewa, ya dauki wadannan matakai bayan da ya tuntubi jam'iyyun siyasa da kwamitin kasa, wato wata hukumar tuntubar juna dake hade da fadarsa. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China