Bisa gayyatar da ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin ta yi musu, zaunannun wakilan kasashe 8 wadanda suka hada da Pakistan da Venezuela da Cuba da Masar da Cambodiya da Rasha da Senegal da kuma Belarus dake Geneva da sauran manyan 'yan diplomasiyyar kasashen, sun ziyarci jihar Xinjiang ta kasar Sin tsakanin ranakun 16 zuwa 19 ga wannan wata, inda suka yi tattaunawar fuska da fuska tsakaninsu da daliban dake karatu a cibiyar koyar da ilmin sana'o'i ta jihar da masu aikin yayata addinin musulunci da kuma sauran mazauna jihar, daga baya sun bayyana cewa, wasu kafofin watsa labarai sun yi karya kan aikin da ake gudanarwa a cibiyar koyar da ilmin sana'o'i ta jihar Xinjiang, haka kuma sun yaba da kokarin da gwamnatin kasar Sin ke yi a fannonin yaki da ta'addanci da kare 'yancin bin addini na 'yan kasar da kuma kiyaye al'adun gargajiyar kananan kabilun kasar.(Jamila)