in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin: Ya kamata kwamitin sulhu na MDD ya sake bita don dage takunkumi kan Sudan
2019-02-26 10:36:13 cri

Wakilin kasar Sin ya yi kira ga kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya, ya sake bitar takunkuman da ya sanya wa kasar Sudan bisa yanayin da kasar take ciki a halin yanzu, sannan daga bisani ya dage takunkuman.

Da yake jawabi a wajen taron kwamitin kan kasashen Sudan da Sudan ta Kudu jiya Litinin 25 ga wata, mataimakin zaunannen wakilin kasar Sin a MDD Wu Haitao, ya ce yanayin tsaro a yankin Darfur na kasar Sudan ya daidaita, bayan rundunar shirin wanzar da zaman lafiya na hadin gwiwa tsakanin MDD da kungiyar Tarayyar Afirka wato AU dake aiki a yankin wato UNAMID, ta mika ragamar tsaron yankin ga jami'an tsaron gwamnatin kasar a bara.

Ya kara da cewa, kasar Sin ta yaba da gudunmuwar rundunar UNAMID wajen wanzar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin na Darfur, sannan tana maraba da gwamnatin kasar Sudan ta yi kokarin inganta tsarin shugabanci da na tsaro.

Ya ci gaba da cewa, a daya bangaren kuma, har yanzu Darfur na fuskantar kalubalen da suka hada da rikicin kabilanci da 'yan gudun hijira da ci gaban zaman takewa da tattalin arziki. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China