Jiya Alhamis 21 ga wata da safe, bisa agogon birnin Washington na kasar Amurka, mataimakin firaministan kasar Sin Liu He, wanda shi ne manzon musamman na shugaba Xi Jinping na kasar Sin, kuma mamban ofishin siyasa na kwamitin tsakiya na JKS, yana jagorantar bangaren Sin a tattaunawar da ke tsakanin Sin da Amurka ta fuskar tattalin arziki daga dukkan fannoni, da kuma Steven Mnuchin, ministan kudi na Amurka sun shugabanci bikin bude tattaunawa a tsakanin manyan jami'ai ta fuskar tattalin arziki da ciniki karo na 7 a fadar White House. Ana gudanar da tattaunawar daga ranar 21 zuwa 22 ga wata a Washington. Bangarorin 2 sun fara aikinsu daga ranar 19 ga wata. (Tasallah Yuan)