in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta yi suka ga rahoton ma'aikatar tsaron Amurka
2019-01-19 16:22:00 cri
Jiya Juma'a, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin madam Hua Chunying ta bayyana cewa, kasarta na nuna rashin jin dadi kan rahoton nazarin tsaron makamai masu linzami da ma'aikatar tsaron Amurka ta bayar a ranar 17 ga wata, inda aka yada jita jita kan barazanar kasar Sin, Hua ta yi gargadi ga Amurka da ta yi watsi da ra'ayin yakin cacar baka, da daukar hakikanan matakai don kiyaye zaman lafiya da zaman karko na kasa da kasa.

Ban da wannan kuma, Hua ta ce, wannan matakin da Amurka ta dauka ko kadan ba shi da ma'ana, zai kuma lahanta zaman lafiya da tsaron shiyya-shiyya, da kawo tasiri ga yunkurin kwace damarar makaman nukiliya, da kuma tayar da gasar jan damara, hakan zai kawo illa ga daidaito da zaman karko a duk fadin duniya.

Hua ta kuma kara da cewa, kullum kasar Sin na tsayawa kan warware matsalar yaduwar makamai masu linzami ta hanyar diplomasiyya kuma a siyasance, da kuma nuna adawa ga hanyar neman tsaro bisa tushen lalata moriyar sauran kasashe.

Baya ga haka, Hua ta ce, Sin zata tsaya kan bin hanyar neman ci gaba cikin lumana, da tsayawa kan manufar tsaron kasa irin ta kare kai, "bata da ra'ayi kuma ba zata kawo barazana ga kasashen duniya ba, ciki har da Amurka." (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China