in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Xi Jinping ya yi shawarwari tare da Kim Jong-un
2019-01-10 10:42:40 cri
A kwanakin baya ne, babban sakatare na kwamitin tsakiya na jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin, kana shugaban kasar, Xi Jinping ya yi shawarwari tare da shugaban jam'iyyar KWP mai mulkin kasar Koriya ta Arewa, Kim Jong-un, wanda ya zo ziyara kasar Sin, inda shugabannin biyu suka yi musanyar ra'ayi da cimma maslaha kan dangantakar dake tsakanin kasashensu da sauran wasu batutuwan da suka jawo hankalinsu.

Xi Jinping ya jaddada cewa, bana aka cika shekaru 70 da kulla huldar jakadanci tsakanin Sin da Koriya ta Arewa, kuma yana fatan yin kokari tare da Kim Jong-un don ciyar da dangantakar kasashen biyu gaba.

A nasa bangaren, Kim Jong-un ya ce, yana fatan amfani da ziyararsa a Beijing a wannan karo don karfafa dankon zumunci tsakanin kasashen biyu, da yin musayar ra'ayi kan karfafa hadin-gwiwarsu, a wani kokari na daukaka ci gaban huldar kasashen biyu.

Har wa yau, bangarorin biyu sun bayyana cewa, za su nuna himma da kwazo wajen daidaita matsalar zirin Koriya ta hanyar siyasa, da kara samar da alfanu ga jama'ar kasashen Sin da Koriya ta Arewa, tare kuma da bayar da gudummawa ga shimfida zaman lafiya da kwanciyar hankali da samar da bunkasuwa a wannan shiyya da ma duk fadin duniya baki daya.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China