in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Nahiyar Afrika na jinkirin sarrafa albarkatun da take da su zuwa abubuwan ci gaba
2018-12-05 10:58:04 cri
Wani rahoto ya bayyana cewa, nahiyar Afrika na jinkiri wajen sarrafa albarkatunta zuwa abubuwan ci gaba, saboda rashin kula da kuma kwarewa.

Rahoton wanda Tarayyar Afrika AU da hadin gwiwar hukumar kula da tattalin arzikin nahiyar Afrika na MDD da shirin raya kasashe na MDD suka hada, ya yi nazari kan kokarin inganta kula da sarrafa albarkatun nahiyar, musamman bukatar karfafa cibiyoyin lura da su da tsarukan inganta samun kudin shiga.

Rahoton kan muradun ci gaba masu dorewa na Arika na 2018, wanda aka gabatar yayin taro kan tattalin arzikin Afrika dake gudana a Kigali babban birnin Rwanda, ya ce bangaren albarkatun wata dama ce ta neman ci gaba ga nahiyar Afrika, baya ga damar samar da kudin gudanar da ayyukan ci gaba, amma kuma yana cike da kalubalen dake bukatar dukkan masu ruwa da tsaki da gwamnatoci da bangarori masu zaman kansu da kungiyoyin al'umma da su yi kokarin sauya tsarin lura da albarkatun. (Fa'iza Msuatpha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China