in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin na fatan sassan da abin ya shafa su dauki matakin da ya dace kan batun nukiliyar Iran
2018-11-05 19:19:22 cri

Yau Litinin kasar Amurka ta maido da takunkumin da ta kakabawa kasar Iran a fannonin makamashi da harkar kudi, wannan shi ne karo na biyu da Amurka ta dauki matakin kan Iran tun bayan da ta fice daga yarjejeniyar nukiliyar kasar ta Iran.

Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Hua Chunying ta bayyana cewa, an daddale yarjejeniyar nukiliyar Iran ne karkashin amincewar kwamitin sulhun MDD, kamata ya yi a aiwatar da ita daga dukkan fannnoni, a don haka kasar Sin tana fatan sassan da abin ya shafa su yi hangen nesa su yi hakuri har su dauki matakin da ya dace.

Jami'ar ta yi wannan tsokaci ne yayin taron ganawa da manema labaran da aka saba yi a nan birnin Beijing.(Jamila)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China