in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An bukaci Guinea-Bissau ta gudanar da zabuka a kan lokaci
2018-10-26 09:26:41 cri

Kungiyar Raya Tattalin Arzikin Kasashen Afrika ta Yamma ECOWAS, da Tarayyar Afrika AU da kuma MDD, sun bukaci kasar Guinea–Bissau ta gudanar da zabukan 'yan majalisar dokokin kasar a kan lokaci kuma bisa adalci da gaskiya.

Cikin wata sanarwar bayan taro ta hadin gwiwa, hukumomin uku sun bukaci masu ruwa da tsaki su hada hannu wajen tabbatar da samar da yanayin da ake bukata don tabbatar da gudanar da zabukan lami lafiya.

Kasar dake yankin yammacin Afrika, ta shirya gudanar da zabukan 'yan majalisar dokokin kasar ne ranar 18 ga watan Nuwamban dake tafe, sai dai ana maganar jinkirta zabukan domin karawa masu kada kuri'a lokacin rajista.

Hukumomin sun kuma yi kira ga kasashen Afrika da sauran kasashen waje, su hada hannu wajen samar da kayayyakin da ake bukata na gudanar da zabukan.

Sanarwar ta kara da cewa, zaben zai zama kari kan nasarorin da kasar ta samu, a don haka, aka fi bukatar goyon bayan al'ummomin kasashen waje fiye da ko yaushe. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China