Kasar Amurka na neman dakatar da shawarwarin da take yi da kasar Sin
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin, Madam Hua Chunying, ta bayyana a yau Talata cewa, a baya kasar Sin da kasar Amurka sun yi shirin gudanar da shawarwari kan harkokin diplomasiyya da aikin tsaro zagaye na 2 a tsakaninsu a tsakiyar watan Oktoban da muke ciki. Amma kasar Amurka a kwanakin baya ta ce tana son dakatar da wannan shawarwarin. Don haka yanzu bangarorin 2 za su ci gaba da tattaunawa dangane da batun shawarwarin. (Bello Wang)
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku