in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugabannin kasar Sin sun halarci bikin murnar cika shekaru 69 da kafuwar kasar Sin
2018-10-01 15:52:37 cri
A daren jiya Lahadi ne majalisar gudanarwar kasar Sin, ta shirya bikin liyafa a nan birnin Beijing, fadar mulkin kasar Sin, don murnar cika shekaru 69 na kafuwar jamhuriyar jama'ar kasar Sin, inda shugaban kasar Xi Jinping, da firaministan kasar Sin Li Keqiang, da sauran shugabannin kasar, gami da wasu baki na kasar Sin, da na kasashen waje fiye da 1200 suka halarci liyafar.

A wajen bikin liyafar, firaminista Li Keqiang ya yi jawabin cewa, tun daga farkon shekarar bana, kasar Sin ta yi kokarin tinkarar wasu kalubalolin da ake samu, sakamakon sauyawar yanayi a ciki da wajen kasar, tare da samun ci gaba a fannin zurfafa gyare-gyare, da kara kokarin bude kofa ga kasashen waje, da kyautata huldar dake tsakaninta da kasashen waje, da karfafa hadin gwiwar da ake yi tare da sauran kasashe.

A cewar firaministan kasar Sin, kasar za ta tsaya kan manufar gyare-gyare a gida, da bude kofa ga kasashen waje, domin gyare-gyaren su ne dalilin ci gaban tattalin arzikin kasar Sin, kana irin ci gaban da ake samu, yana taimakawa wajen daidaita matsalolin da kasar ke fuskanta. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China