in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta sake yin gargadi game da mahaukaciyar guguwar Mangkhut
2018-09-16 15:53:12 cri
Cibiyar ba da bayanai kan hasashen yanayi ta kasar Sin ta bayyana cewa, ana sa ran mahaukaciyar guguwar nan ta Mangkhut za ta isa yankunan dake gabar Zhuhai da Wuchuan na lardin Guangdong dake kudancin kasar yau da rana ko kuma da yamma, kana bayan da isa wadannan yankunan, za ta ci gaba da nausawa zuwa yankin arewa maso yammaci, amma kuma karfinta zai ragu.

A cewar cibiyar, da misalin karfe 5.00 na safe agogon kasar Sin an hango mahaukaciyar guguwar a tekun kudancin kasar Sin kimanin kilomita 420 daga kudu maso birnin Taishan na lardin Guangdong.

Cibiyar ta kara da cewa, yau Lahadi da kuma gobe Litinin yankunan kudancin kasar da suka hada da lardunan Guangdong da Fujian da Hainan, za su fuskanci ruwa da iska mai karfi.

Kasar Sin na da launukan matakan gargadi kan yanayi mai muni guda hudu, kuma launin ja, ya kasance mafi tsanani, sai launin ruwan goro da rawaya da kuma shudi.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China