in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Bankin duniya ya ce kasashen Afrika sun samu dorewar ingancin dabarun tattalin arziki
2018-09-13 10:54:47 cri
Wani rahoton bankin duniya ya ce galibin kasashen Afrika, sun shawo kan matsaloli a ciki da wajen kasashensu, wajen tabbatar da dorewar ingancin dabaru da tsarukan karfafa ci gaban tattalin arzikinsu.

Rahoton da bankin ya fitar jiya a Nairobi, ya ce ma'aunin CPIA na kasashen kudu da hamadar sahara, wanda bankin ke amfani da shi wajen tantance taimakon da zai ba kasashe mafi talauci a duniya da aka kaddamar tun a shekarar 1980, ya ba da sakamako mai kyau game da ingancin dabarun kasashen Afrika, wanda ya bunkasa tattalin arzikin nahiyar.

Babbar mai nazarin tattalin arziki ta Bankin a nahiyar Afrika, Punam Chuhan-Pole, ta ce a shekarar 20017, kasashen Afrika sun samu kyakkyawan yanayi da ya samar musu da damar aiwatar da gyare-gyare.

Ta ce bisa binciken da suka gudanar, kusan kaso 30 na karin wasu kasashe, sun karfafa ingancin dabaru da tsarukansu idan aka kwatanta da shekarar 2016, abun da ta bayyana a matsayin mai karfafa gwiwa.

Rahoton CPIA na 2017, ya yi nazarin ayyukan dabaru da tsarukan tattalin arziki a kasashen Afrika 38, da suka cancanci samun taimakon raya kasa na bankin, wanda ake ba kasashe mafi koma baya ta fuskar tattalin arziki. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China