in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An rantsar da sabbin jagororin gwamnatin Sudan
2018-09-11 10:00:28 cri
Shugaban kasar Sudan Omar al-Bashir, ya jagoranci bikin rantsar da sabbbin shugabannin kasar sa, da suka hada da mataimakin shugaban kasa na farko Bakri Hassan Saleh, da na biyu Osman Mohamed Yousif Kibir, da kuma sabon firaministan kasar Mutaz Mussa.

An dai rantsar da jami'an ne a jiya Litinin, bayan da a ranar Lahadi, jagorancin jam'iyyar NCP mai mulki, ya amince da kudurin shugaban kasar na rushe gwamnatin hadin kan kasa da zabar sabon firaminista, a wani mataki na warware kalubalen tattalin arziki dake addabar kasa.

Gabanin hakan sai da jagororin jami'iyyar ta NCP karkashin jagorancin shugaba al-Bashir suka gana da juna, inda suka tattauna game da bukatar gudanar da sauye sauye ga gwamnatin kasar, tare da gabatar da sunayen wadanda suka cancanta a nada a matsayin sabbin mambobin majalissar zartaswar kasar.

Yayin zaman ne kuma aka amince da nada Mr. Saleh a mataimakin shugaban kasa na farko kadai, bayan da a baya ya taba rike mukamin firaminista da mataimakin shugaban kasa baki daya. Sai kuma Mussa, wanda aka amince da nadin sa a matsayin firaminista, wanda a baya shi ne ministan ma'aikatar noman rani da makamashin lantarki. Kaza lika an amince da nadin Kibir a matsayin mataimakin shugaban kasa na biyu, inda ya maye gurbin Hassabo Mohamed Abdul-Rahman. (Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China