"Muna da shirin da za mu gabatar da shi amma da farko dole ne mu hakikance ainihin abinda muke bukata. Za mu yi amfani da lokacinmu wajen kafa wata ingantacciyar kungiyar 'yan wasa wacce za ta wakilce mu a badi," Seedorf ya bayyana hakan ne a taron manema labarai a Yaounde. Wannan shi ne taron manema labaru na farko da ya gudanar tun bayan da ya sanya hannu kan kwantiragin shekaru 4 da jamhuriyar Kamaru a farkon wannan watan. (Ahmad)