in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An bude makon bunkasa ayyukan masana'antu na kungiyar SADC a matsayin wani dandalin da zai kara dunkule yankin
2018-07-31 10:19:01 cri
An bude makon bunkasa ayyukan masana'antu karo na 3, na kungiyar raya yankin kudancin Afrika SADC, jiya Litinin a Windhoek, babban birnin kasar Namibia, domin samar da dandalin da zai kara hadin kan yankin.

A cewar Tjekero Tweya, Ministan kula da masana'antu da cinikayya da raya sana'o'i na Namibia, taron zai samar da wani dandali da masu kanana da matsakaitan sana'o'i za su baje kolin kayayyaki da hidimominsu.

Ya ce kamar yadda aka sani, dandali irin wannan, na ba kamfanonin dake sana'o'i daban-daban, damar baje sabbin kayayyakinsu da hidimomi, tare kuma da koyon wasu harkokin kasuwanci daga sauran kamfanoni, da nazarin yanayin da kasuwa ke ciki da kuma lalubo damarmakin kasuwanci.

A nasa bangaren, Mataimakin sakataren zartarwa na sashen tabbatar da hadin kan yankin, na kungiyar SADC, Thembinkosi Mhlongo, ya ce rayawa da sauya ayyukan samar da kayyyaki a yankin, na daya daga cikin muhimman abubuwan da kungiyar ta sanya gaba, cikin shirinta na manufofin ci gaba da aka yi wa gyara, na shekarar 2015 zuwa 2020, tare kuma da tsari da manufofin kungiyar na bunkasa ayyukan masana'antu. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China