Rundunar sojojin gwamnatin Somaliya (SNA) tare da masu tallafa musu sun zafafa kaddamar da hare hare domin fattatakar mayakan al-Shabaab a yankin kudancin kasar, sun ce sun yi nasarar kwace manyan yankuna uku daga hannun mayakan a kusa da tashar ruwa ta garin Kismayo.
Mukhtar Abdi Mohamed, shi ne babban kwamandan rundunar SNA a yankin, ya ce an hallaka biyu daga cikin mayakan na al-Shabaab da kuma raunata wasu mayakan uku a lokacin farmakin da sojojin suka kaddamar.
Mohamed ya ce, "Mun yi nasarar kwace yankuna uku, ciki har da yankin Arare wanda a baya yake karkashin ikon mayakan al-Shabaab".
Ya ce, sojojin suna kaddamar da farmakin ne da nufin kwato muhimman yankunan dake karkashin kungiyoyin 'yan ta'addan wadanda ke kaddamar da hare hare kan dakarun gwamnatin Somaliya a kullum, ya kara da cewa, za su ci gaba da aiki har zuwa lokacin da dakarun na SNA da na jihar Jubaland za su kwato dukkan yankunan daga hannun mayakan.(Ahmad Fagam)