in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta taya wa Kango Kinshasa murnar kawo karshen cutar Ebola a kasar
2018-07-18 20:32:08 cri
Yau Laraba, mai magana da yawun ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin, Hua Chunying ta bayyana cewa, an kawo karshen annobar cutar Ebola baki daya wadda ta barke a watan Mayun bana a Jamhuriyar Demokuradiyyar Kango, kuma kasar Sin ta taya kasar murnar samun babbar nasara wajen yaki da annobar.

Rahotannin da aka ruwaito sun ce, ma'aikatar lafiya ta Jamhuriyar Demokuradiyyar Kango ta sanar da cewa, an dasa aya ga annobar Ebola wadda ta barke tun watan Mayun shekarar da muke ciki. Madam Hua ta ce, ba tare da wani jinkiri ba, kasar Sin ta bada kyautar tufafin kariya, da marufin hanci da baki, gami da safar hannu ga kasar Kango Kinshasa, ta kuma samar mata da tallafin jin-kai. Haka kuma, likitoci kwararru na kasar Sin sun je kasar Kango Kinshasa a farkon watan Yuni, don taimaka mata shawo kan yaduwar cutar Ebola.

Madam Hua ta jaddada cewa, matakan da kasar Sin ta dauka sun shaida irin dankon zumunci, da kyakkyawan hadin-gwiwa da dangantaka tsakanin kasar Sin da Jamhuriyar Demokuradiyyar Kango, har ma da duk nahiyar Afirka baki daya, abun da ya samu babban yabo daga gwamnatin kasar, gami da kasashen duniya daban-daban.

Kasar Sin za ta ci gaba da taimakawa kasashen Afirka wajen inganta kwarewarsu ta fuskar yaki da yaduwar cututtuka, da karfafa tsarin kiwon lafiyar jama'a.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China