in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin za ta kara tallafawa aikin kiyaye zaman lafiya
2018-06-22 13:33:19 cri
Wani babban jami'in hukumar 'yan sandan kasar Sin ya yi alkawarin cewa, kasarsa za ta kara kokarin tallafawa aikin kiyaye zaman lafiya da MDD ke gudanarwa a kasashe daban daban.

Wang Xiaohong, mataimakin shugaban hukumar 'yan sandan kasar Sin, ya yi furucin ne, a jiya Alhamis, a wajen taron shugabannin 'yan sandan duniya karo na 2 na MDD, wanda ke gudanar a hedkwatar majalissar dake birnin New York.

Jami'in na kasar Sin ya ce, kasarsa za ta kara zuba ma aikin kiyaye zaman lafiya jari, da gudanar da kwas na horar da ma'aikata, da tura kwararru masu horaswa bisa hadin gwiwa da MDD. Kana, a cewarsa, za a bada muhimmanci ga shirin horar da ma'aikata a nahiyar Afirka, don cimma burin da aka sanya na horar da 'yan sandan kiyaye zaman lafiya 1000. Ya ce, a shirye kasar Sin take, wajen kokarin taimakawa kasashen Afirka karfafa ayyukan tsaro da shari'a, karkashin tsare-tsaren da MDD ta tanada. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China