in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Najeriya ya hori Super Eagles da su daukowa kasar kofin duniya
2018-05-31 09:22:50 cri
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya hori babbar tawagar 'yan wasan kwallon kafan kasar wato Super Eagles, da su zage damtse wajen daukowa kasar lambar zinare a gasar da za'a gudanar a watan gobe na cin kofin duniya na hukumar FIFA a kasar Rasha.

A lokacin da yake karba bakuncin tawagar 'yan wasan a Abuja fadar mulkin kasar, shugaban Buhari, ya kuma bukaci 'yan wasan dasu gudanar da ingantaccen wasa mai tsabta a wasan cin kofin duniyar.

Tawagar 'yan wasan ta Super Eagles zata yada zango ne a Ingila a ranar Laraba da zarar ta kammala ganawa da shugaba Buhari a fadar shugaban kasar a gaban wasu daga cikin mambobin majalisar zartaswar kasar da jami'an hukumar wasan kwallon kafan kasar.

Zasu gudanar da wasan sada zumunta da kungiyar wasan Three Lions ta Ingila a filin wasan Wembley a ranar 2 ga watan Yuni gabanin su halarci gasar cin kofin duniyar.

German Gernot Rohr, kociyan kungiyar wasan, zai zabo 'yan wasa 23 bayan kammala wasan sada zumuntar da zasu gudanar a ranar Asabar, wanda za'a mika sunayen ga hukumar shirya wasan kwallon kafan ta duniya a ranar Litinin.

Buhari ya bukaci Super Eagles dasu yi amfani da kuruciyarsu wajen taka rawar gani a gasar ta FIFA.

Najeriya zata fafata da Croatia, Iceland, da kuma Argentina a rukunin D. (Ahmad)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China