in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Habasha ta musanta zargin da Eritrea ta yi mata na marawa 'yan tawaye baya
2018-05-21 10:10:44 cri

Ma'aikatar harkokin wajen Habasha, ta ce zargin kasar da Eritrea ta yi na mara baya ga 'yan tawayen Eritrean, ba shi da tushe.

A ranar Laraba da ta gabata ne, ministan labarai na Eritrea, ya fitar da sanarwar da ta zargi makwabtan kasashen, da suka hada da Sudan da Habasha, da hada baki don taimakawa kungiyoyin 'yan tawaye dake kasar.

Sanarwar ta Eritrea, ta kuma ce Habasha da Sudan, sun amince su tura 'yan tawayen na Eritrea zuwa kan iyakokinsu da kasar, domin saukaka musu kai hari kasar da tsarewa.

Da yake ganawa da kamfanin dillancin labarai na Xinhua, kakakin ma'aikatar harkokin wajen Habasha Meles Alem, ya ce zargin na Eritrea karya ne tsagwaronta.

Ya kuma ce, har yanzu, Habasha na kan bakanta na tattaunawa da sulhuntawa da Eritrea ba tare da sharadi ba, duk kuwa da takkadamar dake tsakaninsu. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China