in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Bankin duniya ya ce ci gaban tattalin arzikin Afirka ya dogara kan sauye sauye a fannin ilimi
2018-04-27 10:08:21 cri

Jami'ar babban bankin duniya mai lura da harkokin raya ilimi a gabashin Afirka Sajitha Bashir, ta ce ci gaban nahiyar Afirka ta fuskar tsaro da zaman lafiya, da bunkasar tattalin arziki, ya ta'allaka kacokan kan irin sauye sauye da nahiyar ta aiwatar a fannin raya ilimi.

Sajitha Bashir, ta bayyana hakan ne a jiya Alhamis, a gefen taron karawa juna sani na masu ruwa da tsaki a fannin raya ilimin nahiyar, wanda ya gudana a birnin Nairobin kasar Kenya. Ta ce, managarcin tsarin samar da ilimi, zai tallafawa nahiyar wajen yin takara a fannin bunkasar tattalin arziki, tare da samar da dama ta magance kalubalen zamantakewa da na siyasa da nahiyar ke fama da su.

Mahalarta taron dai sun hada da ministocin ilimi na kasashen Afirka, da masu tsara manufofi, da wakilan manyan hukumomin kasa da kasa, da masu rajin bunkasa ilimi. Dukkanin sassan dai sun amince da muhimmancin dake tattare da bunkasa ilimi, a matsayin hanyar fadada ci gaban nahiyar baki daya.(Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China