in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin ya yi maraba da dakatar da gwajin makaman nukiliya da Koriya ta Arewa ta yi
2018-04-21 16:20:54 cri
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Lu Kang, ya bayyana a yau cewa, kasar Sin ta yi maraba da kudurin dakatar da gwajin makaman nukiliya da harba makamai masu linzami da jam'iyyar kwadago ta kasar Koriya ta Arewa ta yi, tare da daukar niyyar kokarin raya tattalin arziki da inganta zaman rayuwar jama'ar kasar.

Lu Kang ya bayyana cewa, a ganin kasar Sin, kudurin da Koriya ta Arewa ta yanke, zai taimaka wajen sassauta halin da ake ciki a zirin Koriya, da sa kaimi ga warware batun kawar da makaman nukiliya a zirin Koriya da matsalar zirin Koriya ta hanyar siyasa.

Cimma burin kau da makaman nukiliya da samun zaman lafiya mai dorewa a zirin Koriya ya dace da moriyar zirin Koriya da jama'ar dake yankin, har ma da sauran kasashen duniya.

Lu Kang yana fatan bangarori daban daban da abin ya shafa za su cimma daidaito, tare da daukar matamai don yin kokarin cimma burin samun zaman lafiya mai dorewa da ci gaba a yankin, ya na mai cewa Kasar Sin za ta ci gaba da taka muhimmiyar rawa kan batun. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China