Yau Talata ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya gana da takwaransa na kasar Koriya ta Arewa Ri Yong Ho, wanda ya yada zango a nan birnin Beijing. Bangarorin 2 sun yi nuni da cewa, za a aiwatar da ra'ayi daya da shugabannin kasashen 2 suka cimma, tare da kara ziyartar juna tsakanin manyan jami'ai, da inganta tuntubar juna a matakai daban daban, a kokarin ci gaba da raya huldar abokantaka a tsakanin kasashen 2. (Tasallah Yuan)