in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta dauki matakan kara habaka bude kofa ga kasashen ketare ne da nufin sada kasashe daban daban da moriyar saurin ci gabanta
2018-04-12 19:45:24 cri
Kakakin ma'aikatar kasuwanci ta kasar Sin ya bayyana a yau Alhamis cewa, matakan kara habaka bude kofa ga kasashen ketare da Sin ta sanar a kwanan baya, babbar manufa ce da kasar ta tsara bisa ga kimanta matsayin ci gaba da kasar ke ciki, domin ba ta damar kyautata matsayin ta na bude kofa ga kasashen ketare a sabon zamani, hakan kuma domin samun ci gaban kanta.

Kwanan baya, kasar Sin ta sanar da cewa, za ta dauki karin muhimman matakai, a fannonin fadada hanyoyin shiga kasuwanninta, da kara habaka shigar da kayayyaki da dai sauransu.

Game da hakan, kakakin ma'aikatar cinikayyar kasar Sin Gao Feng, ya bayyana a yayin taron manema labaru da aka yi a yau cewa, a cikin shekaru 40 da suka gabata, tun fara gudanar da yin kwaskwarima a cikin gida da bude kofa ga kasashen ketare, kasar Sin ta cimma gagarumar nasara. Don haka, ana iya fahimtar cewa, muddin kasar Sin ta aiwatar da manufar yin kwaskwarima a cikin gida da bude kofa ga kasashen ketare, za ta iya tabbatar da ci gabanta. Don haka, bisa son ranmu ne muke sanar da wadannan matakai na kara bude kofa ga kasashen waje, ta yadda kuma kasashen ketare za su amfana daga bunkasuwar tattalin arzikin kasar Sin.(Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China