in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jakadan kasar Sin a Amurka ya bukaci Amurka da ta daina bincike mai lamba 301 kan kasar Sin
2018-04-05 12:30:09 cri

Jiya Laraba jakadan kasar Sin da ke kasar Amurka Cui Tiankai, ya gana da mukaddashin sakataren harkokin wajen kasar Amurka John J. Sullivan a birnin Washington DC., inda suka yi musayar ra'ayoyi kan huldar da ke tsakanin kasashen 2, da sauran batutuwa.

A yayin ganawar tasu, mista Cui Tiankai, ya sake nanata matsayin kasar Sin dangane da batun tattalin arziki da ciniki a tsakaninta da Amurka. Ya kuma bukaci Amurka da ta yi watsi da ra'ayin kashin kai, da matakin ba da kariya kan harkokin ciniki cikin hanzari, ta kuma sa aya ga bincike mai lamba 301 da take yi kan kasar Sin, kana ta hada kai da kasar Sin wajen daidaita wannan sabani ta hanyar shawarwari da tattaunawa. (Tasallah Yuan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China