Rahoto: Rikici da matsalar yanayi su ne manyan dalilan dake haddasa karancin abinci
Kungiyar yanar gizo mai ba da bayanai game da wadatar abinci, ta ce sakamakon rikicin siyasa da bala'i daga Indallahi a fannin yanayi, ya sa yawan mutanen da suke fama da yunwa ya karu da kashi 15% a bara.
Kungiyar ta bayyana haka ne cikin wani rahoto da ta gabatar dangane da matsalar karancin abinci a duniya, a birnin Rome na kasar Italiya a jiya Alhamis, inda ta kara da cewa, matsalar na kara tabarbarewa.(Bello Wang)