in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sakataren harkokin wajen Amurka zai yi rangadi karon farko a kasashen Afrika 5
2018-03-02 10:12:53 cri
Ma'aikatar harkokin wajen Amurka ta ce Sakataren harkokin wajen kasar Rex Tillerson, zai kai ziyara kasashen Afrika 5 daga ranar 6 zuwa 13 ga watan Maris.

Cikin wata sanarwar da ya fitar, kakakin ma'aikatar Heather Nauert, ya ce rangadin da Rex Tillerson zai yi a karon farko, zai kai shi Chadi da Djibouti da Habasha da Kenya da kuma Nijeriya.

Yayin rangadin, Sakataren zai gana da shugabannin kasashen da kuma shugabancin Tarayyar Afrika dake da mazauni a birnin Addis Ababa na Habasha, a yunkurin Amurka na kulla kawance da gwamnatoci da al'ummar Afrika.

Takamaimai dai, Rex Tillerson na da shirin tattauna hanyoyin da Amurka da nahiyar Afrika za su yi aiki tare, wajen yaki da ta'addanci da wanzar da tsaro da zaman lafiya da inganta shugabanci na gari da kuma lalubo damarmakin ciniki da zuba jari da bangarorin biyu za su ci gajiya. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China