in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wakilin ofishin siyasa na kwamitin tsakiyar JKS zai kai ziyara Amurka
2018-02-06 09:27:43 cri
Jiya Litinin, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Geng Shuang ya sanar da cewa, bisa gayyatar da ministan harkokin wajen kasar Amurka Rex Tillerson ya yi masa, wakilin ofishin siyasa na kwamitin tsakiyar Jami'iyyar Kwaminis ta Kasar Sin, kana wakilin majalisar gudanarwar kasar ta Sin Yang Jiechi, zai yi ziyarar aiki a kasar Amurka a ranekun 8 da 9 ga watan nan da muke ciki.

Haka kuma, ya ce, kasashen Sin da Amurka sun nuna aniyarsu wajen karfafa shawarwarin dake tsakaninsu bisa fannoni daban daban. A yayin ziyarar Yang Jiechi a kasar Amurka, zai yi tattaunawa da jami'an kasar game da dangantakar dake tsakanin Sin da Amurka, da wasu batutuwan kasa da kasa dake janyo hankulan kasashen biyu. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China